Japan: Jam'iyyar LDP na kan gaba a zaben majalisar dokoki
February 8, 2026
Talla
Sakamakon farko na zaben 'yan majalisar dokokin Japan na nuna cewa jam'iyyar Firanminista Sanae Takaichi ta LDP za ta lashe kujeru mafi yawa cikin 465 na majalisar kasar, hasalima jam'iyyar da kawayenta na iya lashe kaso 2 bisa 3 na kujerun kamar yadda kafar watsa labaran kasar ta NHK ta rawaito.
Karin bayani: An bude runfunan zaben 'yan majalisar dokoki a Japan
Jam'iyyar LDP ta mulki Japan a lokuta mafi yawa cikin shekaru 70, sai dai kuma ta rasa rinjaye a majalisar kasar sakamakon dambarwar siyasa da ta kunno kai.