1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: An jingine matakin dta aka dauka kan Jam'iyyar AfD

May 8, 2025

Hukumar leken asiri a Jamus, ta jingine matakinta a kan jam'iyyar nan ta AfD mai kyamar baki da wasu tsare-tsaren gwamnati, jam'iyyar da aka nunar da cewa tana yi wa dimukuradiyya karan tsaye.

Gangamin 'yan jam'iyyar AfD kafin zabe a jihar Saxony a 2024
Gangamin 'yan jam'iyyar AfD kafin zabe a jihar SaxonyHoto: Michaela Stache/AFP/Getty Images

Hukumar leken asiri ta kasar Jamus, ta jingine matakinta na ayyana jam'iyyar nan ta masu ra'ayin rikau a matsayin mai matsanancin ra'ayi watau AfD, matsayar da ta bayyana a kanta a makon da ya gabata.

Jinginewar hukumar za ta ci gaba ne har sai kotu ta yanke hukunci kan korafin da AfD ta shigar.

Wannan dai wani bangare na ci gaba a cewar jam'iyyar ta AfD, wadda ake ganin tana da akidu masu tsauri ciki har da na kyama ga baki.

Matakin hukumar leken asirin Jamus din na bayyana jam'iyyar a matsayin mai matsananci ra'ayi, ya janyo suka ciki kuwa har da gwamnatin Donald Trump ta Amurka.

Wasu dai daga cikin 'yan majalisar dokokin Jamus, sun bukaci da haramta jam'iyyar kwata-kwata, saboda abin da suka kira da tabargazarta ga tsari na dimukuradiyyar kasar.