1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta taimakawa sake gina Siriya bayan yakin basasa

Zainab Mohammed Abubakar
June 18, 2025

Ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul ya bayyana cewa, kasashen Jamus da Siriya sun amince da kafa wata majalisar tattalin arziki na hadin gwiwa.

Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Wannan majalisa na da nufin tallafawa sake gina kasar bayan shafe fiye da shekaru goma ana yakin basasa.

Wadephul, wanda ya ce sun amince da matakin da takwaransa na Siriya Asaad al-Shaibani yayin wata tattaunawa ta wayar tarho, ya ce ofishin kula da harkokin wajen Jamus zai gudanar da ayyukan majalisar.

Tun da farko dai babban jami'in diflomasiyyar na Jamus ya shirya kai ziyara birnin Damascus a ranar asabar da ta gaba, sai dai kaddamar da manyan hare-haren da  Isra'ila ta yi a kan Iran a ranar Juma'a, ya tilasta masa dakatar da tafiyar.