Jamus: Dan bindiga ya bude wuta kan jama'a
January 24, 2020!['Yan sanda a wurin da aka yi harbe-harben da ke a garin Rot am See](https://static.dw.com/image/52140604_800.webp)
Talla
Harin bindigar da 'yan sanda suka danganta shi da na kashin kai ya yi sanadiyyar mutuwar mutane shidda tare da jikata wasu da dama. Jami'an 'yan sanda a garin Rot Am See da ke jihar Baden-Würtemberg na kudancin Jamus suka fidda wannan sanarwar a shafinsu na Twitter.
Har wayau sanarwar ta kara da cewar tuni aka damke mutum guda da ake zargi da kai harin, sai dai ba a kai ga sanin ko shi kadai ne ya kai harin ba da ma dalilansa na aikata wannan ta'asa.