1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Jam'iyyar CDU ta Merz ta yi rawar gani a zabe

Abdullahi Tanko Bala
September 14, 2025

Yayin da Jam'iyyar CDU ke kan hanyar nasara, Jam'iyyar AfD mai kyamar baki ta rubanya yawan kuri'iun da ta samu a baya a Jihar North Rheine-Westphalia, jiha mafi yawan al'umma a Jamus

Zaben kananan hukumomi da Magadan gari a Jamus
Zaben kananan hukumomi da Magadan gari a JamusHoto: Christoph Hardt/Panama Pictures/picture alliance

Yayin da aka rufe rumfunan zabe a fadin Jihar North Rhine-Westphalia, jiha mafi girma a Jamus a zaben kananan hukumomi da na magadan gari, hasashen sakamakon farko ya nuna Jam'iyyar CDU ta shugaban gwamnati Friedrich Merz na shirin samun nasara, sai dai jam'iyyar kyamar baki ta AfD ita ma tana cikin shaukin murna.

Jam'iyyar CDU ta Merz ana sa ran za ta sami kashi 34 cikin dari na kuri'iun da aka kada, Sai Jam'iyyar SPD da ke biye mata da kashi 22.5 cikin dari sai kuma AfD mai kyamar baki da ke da kashi 16.5 cikin dari inda ta rubanya har sau uku sakamakon da ta sami na kashi 5.1 cikin dari a zaben 2020.

Zaben na wannan lahadin shi ne na farko da aka gudanar tun bayan da Friedrich Merz ya hau karagar mulki a matsayin shugaban gwamnati a watan Mayu.

AfD ta sami gagarumar nasara a shekarun baya bayan nan inda ta zama jam'iyya ta biyu mafi karfi a kasa baki daya. Ko da yake magoya bayanta sun fi karfi a gabashin Jamus amma ta na fatan motsawa a yammacin Jamusa.