1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Jamus ta yi kakkausar gargadi a kan corona

November 22, 2021

Ministan lafiyar Jamus Jens Spahn ya gargadi mutanen kasar  da su kara kaimi wurin karbar rigakafin corona. Sphan ya ce zuwa karshen hunturu na bana, corona za ta iya halaka wadanda ba su yi rigakafi ba.

Weitere Entwicklung in der Corona-Pandemie
Hoto: picture alliance/dpa

Gargadin da ministan ya yi a wannan Litinin na zuwa ne a yayin da corona ta sanya Jamus a gaba a cikin 'yan makonnin nan, har ta kai ga duk da ingancin tsarin kiwon lafiyar kasar, asibitoci ke gargadin cewa sun fara tunbatsa da mutanen da corona ta yi wa mugun kamu.

Mutane sama da miliyan biyar cutar ta kama, a cikinsu kuma ta yi ajalin kusan mutum 100,000 tun daga farkon fara annobar a duniya.