1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta bi sahun neman a dakatar da yaki a Sudan

November 1, 2025

Jamus ta shiga sahun kasashen duniya da ke kiran da a gaggawar tsagaita wuta a yakin da ke ci a Sudan. Smaa da shekaru biyu ke nan da Sudan ke fama da yakin da ya daidaita fararen hula baya ga asarar rayuka.

Sudan El-Fasher 2025 | ‘Yan tawayen RSF na murnar kwace iko da birnin El-Fasher a Darfur
‘Yan tawayen RSF na murnar kwace iko da birnin El-Fasher a DarfurHoto: Rapid Support Forces/AFP

Ministan harkokin wajen Jamus, Johann Wadephul, ya bayyana halin da Sudan ke ciki a matsayin mummunan bala’i, yana mai cewa babbar matsalar jinkai ta duniya a yanzu ta tare a Sudan din.

A taron da aka gudanar a Bahrain, kasashen Burtaniya da Jordan su ma sun yi magana kan rikicin, suna kiran da a kawo karshen tashin hankalin.

Tun watan Afrilu 2023, dakarun rundunar RSF ke fafatawa da sojojin gwamnati.

A karshen makon da ya gabata, RSF ta kori rundunar soji daga sansanin ta na karshe a yammacin Darfur.

Rahotanni daga garin El-Fasher sun bayyana cewa ana samun kashe-kashe ba tare da shari’a ba, da fyade da fashi da ma hare-hare kan ma’aikatan agaji.