Jamus ta rufe ofishin jakadancinta a Kabul
October 18, 2013Talla
Ministan tsaron tarayyar ta Jamus Thomas de Maiziere ne ya bayyana hakan a wannan Juma'ar a birnin Berlin inda ya kara da cewar sun yi gaggawar yanke wannan hukunci ne saboda labarin da suka samu cewar shirye-shiryen kai harin sun yi nisa.
Shi kuwa mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Jamus din Martin Schaefer ya shaidawa kamfanin dillacin labari na Jamus na Dpa cewar Jamus din ta yanke hukuncin rufe ofishin nata na jakadanci a Kabul din ne domin ta kare 'yan kasarta daga duka wani hari na ta'addanci.
Yanzu haka dai an dakatar da duk wani aiki a ofishin kamar dai yadda jaridar Die Welt da ake bugawa a nan Jamus ta shaida a daren jiya Alhamis.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammed Awal Balarabe