1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Larabawa sun sayi makamai daga hannun Jamus

January 3, 2021

Gwamnatin Jamus ta sayar wa da kasashen Gabas ta Tsakiya makaman yaki da kudin su ya haura miliyan 1000 a shekarar da ta gabata ta 2020.

Ägypten Merkel und al-Sisi
Hoto: Reuters/Amr Abdallah Dalsh

Kamfanin dillancin labarai na DPA ya ce kasashen da ke cikin rikicin Libya da Yemen su ne galibi suka fi sayen makaman daga hannun Jamus. Kasar Masar wace ta sayi makamai na Euro miliyan 752 ita ce ke kan gaba sai Qatar wace ta sayi makamai na Euro miliyan 305. Akwai kuma kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Kuwait da Turkiyya da su ma suka sayi makamai a hannun Jamus din. Ma'aikatar tattalin arzikin Jamus dai ta fito da wadannan bayanai ne bayan da wani dan majalisar kasar ya bukaci ta yi wa jama'a bayani dalla-dalla. Jamus din na cikin kasashe biyar na duniya da suka yi suna wurin kera makamai da sayar da su a duniya. Akwai Rasha da Amirka da Faransa da kuma China da su ma ke sayar da makaman yakin.