1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta taimaki Mali da Euro miliyan ɗaya

November 1, 2012

Ministan harakokin wajen Jamus Guido Westerwelle ya gana da hukumomin Mali albarkacin ziyarar da ya kai a Bamako babban birnin kasar.

Außenminister Guido Westerwelle (FDP, 2.v.r.) spricht am 01.11.2012 auf dem Flughafen in Bamako in Mali mit dem Minister für Auswärtige Angelegenheiten und internationale Zusammenarbeit der Republik Mali, Tiéman Hubert Coulibaly. Westerwelle informiert sich bei seinem dreitägigen Besuch in Afrika über die Lage, nachdem Islamisten Teile Malis unter ihre Kontrolle gebracht haben. Foto: Michael Kappeler/dpa +++(c) dpa - Bildfunk+++
Ministan harkokin wajen Mali Tiéman Hubert Coulibaly ya tarbi WesterwelleHoto: picture-alliance/dpa

Ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle, ya kai ziyarar aiki a ƙasar Mali inda ya gana da hukumomin Bamako game da hanyoyin samar da zaman lafiya.

Westerwelle ya yi amfani da wannan dama, inda ya ba da albishirin tallafin tsabar kuɗi Euro miliyan ɗaya a matsayin agajin Jamus ga al'umar Mali da ta shiga mawuyacin hali sakamakon rikicin da ƙasar ke fama a shi. Jamus ta buƙaci ayi amfani da wannan kuɗaɗe, ta fannin samar da abinci, kiwon lafiya da kuma taimakawa mutanen da ambaliyar ruwa ta rutsa da su.

A ɗaya wajen, Jamus ta yi tayin ba da ɗauki domin ƙwato yankin arewancin Mali da a halin yanzu ke cikin hannun ƙungiyoyi masu tsatsauran kishin addinin Islama.

Asarid Ag Ibarkawane shine mataimakin shugaban Majalisar dokokin Mali na buiyu, ya baiyana mahimmancin dangantaka tsakanin Jamus da Mali:

Jamus itace ƙasar farko da ta amince da samun 'yancin kan ƙasar Mali.Kasashen biyu na da alaƙar ƙut da ƙut.Wannan dama ce muka samu, domin baiyanawa minista Westerwelle inda aka kwana, a yunƙurin warware rikicin ƙasar Mali, sannan mu ji irin tallafin da ƙasarsa ka iya badawa domin cimma burin da aka sa gaba.

Bayan ganawa da hukumomin Mali, a ɗaya wajen Guido Westerwelle ya tattauna da ƙungiyoyin farar hula game da batun aika rundunar ƙasa da ƙasa a yankin arewacin Mali.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Zainab Mohammed Abubakar