1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta kafa rundunar tsaro mai karfi

Abdullahi Tanko Bala
May 14, 2025

A Jawabin da ya yi wa majalisar dokokin tarayya, shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya zayyana fannonin da gwamnatinsa za ta fi bai wa fifiko da suka da farfado da tattalin arzikin kasar da mayar da ita mai tasiri

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz
Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya ce sabuwar gwamnatinsa ta hadaka za ta bayar da fifiko kan tsaro da hadin kai da kuma raya ci gaba. Ya ce domin cimma wannan buri akwai bukatar sauyin manufofi ta fuskoki da dama.

Ya baiyana hakan ne yayin jawabinsa na farko a gaban majalisar dokokin tarayya a Berlin. Merz ya ce sabuwar gwamnatin wadda ta kunshi Jam'iyyun CDU da abokan kawancensu na Bavaria CSU da kuma Jam'iyyar SPD suna sane da kalubalen da Jamus ke fuskanta na cikin gida da waje musamman matsalolin kudade. Ya ce Jamus ta na karfi da juriya kuma za ta shawo kan kalubalen.

A waje guda kuma shugaban gwamnatin Friedrich Merz ya bukaci kasashen Turai cewa kada su yarda su rarraba akan Ukraine. Ya ce yana kokarin tabbatar da hadin kai tsakanin Turai da Amurka kan yadda za a kawo karshen yakin.