1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta mayar wa Najeriya da kayan tarihi

Binta Aliyu Zurmi MAB
December 15, 2022

Mahukunta a birnin Cologne na kasar Jamus sun amince da mayar wa Najeiya da wasu kayayakin tarihi da aka sace a masarautar Benin tun lokacin mulkin mallaka na Turawan Birtaniya.

Mahukunta Najeriya da Jamus a yayin yunkurin mayar wa Najeriya da kayayyakin tarihiHoto: Julia Hinz/DW

Darakta janar na hukumar adana kayayakin tarihi na Najeriya Abba Isa Tijani na daga cikin wadanda suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar mayar wa Najeriya kere-keren tagulla da suka fito daga masarautar gargaji ta Benin a 1897. Amma Jamus ta shirya mayar da wadannan kayayyakin Najeriya a shekarar 2023 mai zuwa kamar yadda gwamnatin Jamus din ta sanar. 

Ko baya ga kayayyakin tarihin masaurautar Benin, akwai wasu da yawansu ya haura dubu da dari daya da ke jibge a gidajen adana kayayakin tarihi 20 a Jamus. Sai dai bangarorin biyu sun cimma yarjejeniyar bar wa birnin Cologne wasu kayayakin tarihi 37 a matsayin aro na tsawon shekaru 10.