Jamus:Za a yi shari'ar wadanda suka kitsa juyin mulki a kotu
April 1, 2026
Mutanen nan uku masu tsatstsauran ra'ayi da gwamnatin Jamus ke zargi da yunkurin juyin mulki da kuma kitsa sace minista, za su gurfana gaban kotun birnin Munich a ranar Laraba.
A 2025 babbar kotun birnin Koblenz ta yanke wa mutanen uku tare da wata mace guda daya hukuncin dauri, tsakanin shekaru takwas da shekaru biyar da kuma watanni tara.
Karin bayani: Jamus ta jaddada yunkurinta na mayar da bakin haure 'yan Siriya a gida
Mutanen sun hada da Achim M mai shekaru 60 da Joachim K mai shekaru 71 da kuma Rainer S mai shekaru 62, wadanda ake zargi da kitsa yin garkuwa da ministan lafiya na lokacin Karl Lauterbach, kan matakansa na lokacin cutar Corona, bisa kudurinsu shirya juyin mulki.
Karin bayani:Rikicin Sudan ya dauki hankulan jaridun Jamus
Ko a cikin watan Nuwamban 2025, 'yan sanda sun kama wani mai alaka da mutanen, wadanda ake kiran kungiyarsu da Reichsbuerger, bayan wasu jawabai da ya wallafa a shafukan sada zumunta da ke ikirarin shirin kashe 'yan siyasa, ciki har da tsohuwar shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da magajinta Olaf Scholz.