Cece-kuce bayan karin kudin mai a Najeriya
May 12, 2016Gwamnatin Najeriyar karkashin jagorancin Muhammadu Buhari mai taken canji ta yi wa batun tallafin man fetir din Najeriyar da ke cike da takaddama kifa daya kwala, inda ta sanar da janye tallafin tare da yin karin farashin daga Naira 86.50 zuwa Naira 145, abin da ya nina kari na sama da kashi 80 cikin 100.
Gwamnatin na mai dagewa kan cewar wannan zai sanya wadatuwar man fetir din da ‘yan Najeriya suka kwashe watanni na fama da karancinsa. To sai dai kungiyar kwadagon kasar da ta dade da adawa da duk wani yunkuri na janye talafi, ta ce ba fa za ta sabu ba kamar yadda Comrade Nuhu Toro mai taimaka wa shugaban kungiyar kwadagon Najeriya ya bayyana.
Karin farashin mai dai a Najeriya a kowane lokaci kan fuskanci martani na bai daya daga al'ummar kasar, musamman saboda yadda lamarin kan shafi rayuwar talaka, amma a wannan karon da alamun ra'ayoyi na shan bam-bam tsakanin ‘yan Najeriyar kamar yadda wasu suka bayyana a Abuja.
To amma ga Mustapha Fanandas daya daga cikin matsan jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya na mai bayyana adawarsu da wannan kari. A ranar Jumma'a ce dai kungiyar kwadago a Najeriyar ke shirin taro wanda talakawan kasar ke jira su ga yadda za ta kaya.