Tuni da hari da makamin kare dangi na Hiroshima
August 6, 2020![Japan I Zeremonie zum Jahrestag in Hiroshima](https://static.dw.com/image/54456295_800.webp)
A yau shida ga watan Augusta ake cika shekaru sabain da biyar (75) da faruwar harin Hiroshima da Nagasaki na kasar Japan, Amirka ta soma jefa makamin Nukiliya na kare dangi a birnin Hiroshima kafin ta jefa na biyun a Nagasaki, lamarin da ya sa Japan mika wuya a yayin yakin duniya na biyu.
Al'umomin a kasar kan hadu a duk rana irinta ta yau don nuna alhini kan iftala'in da yayi sanadiyar rayukan Japanawa kimanin dubu dari da arba'in, amma a bana, annobar Corona ta rage ma taron da ke hada kan 'yan kasa dama baki daga kasashen duniya armashi.
Firaiminista Shinzo Abe a yayin jawabinsa, ya ce, kasar za ta yi duk mai yiyuwa wajen ganin an haramta amfani da duk wani na'ui na makamin nokiliya. Tarihi ya nuna cewa, hare-haren na Hiroshima da Nagasaki sun kasance karon farko da ake kai hari da makami mai guba kan bil'adama a duniya.