1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jawabin Obama kan hukuncin kashe Martin

July 15, 2013

Shugaba Barack Obama ya yi kira ga al'uma da su kwantar da hankulansu bayan da kotu ta wanke Zimmermen da ya kashe wani matashi bakar fata mai suna Trayvon Martin.

Barack Obama hält zum Abschluss seiner Reise eine politische Grundsatzrede an der Universität Kapstadt. Südafrika, den 30. Juni 2013. zugeliefert von: Ludger Schadomsky copyright: DW/Ludger Schadomsky
Barack Obma Rede an Universität in KapstadtHoto: DW/L. Schadomsky

Obama ya ce ko da ya ke wannan shari'a ta tayar da hankulan jama'a a Amirka, amma ya zamo wajibi a amince da hukuncin da kotun ta yanke. Shugaban ya kara da cewa ko da yake Amirka kasa ce mai bin doka, to amma akwai ayar tambaya game da hanyar da ta dace a bi domin kawar da sake aukuwar wannan danya. Obama ya fadi haka ne ya na mai nuni da shirinsa na tsananta dokar mallakar makamai.

A watan Fabarairu na shekarar 2012 ne dai George Zimmerman, wanda a wancan lokaci ya ke aikin sa kai na tsaro ya harbe Trayvon Martin a unguwar Sanford da ke jihar Florida. Shi dai Zimmerman mai asali daga Latin Amirka ya ce ya yi hakan ne domin kare kansa. Sai dai masu shigar da kara sun dora masa laifin aikata kisa. Ko shakka babu wannan shari'a za ta janyo tafka muhawara a kan wariyar jinsi a Amirka ..

An dai shirya gudanar da zanga -zanga a duk fadin kasar ta Amirka domin nuna rashin amincewa da hukuncin da kotun ta tyanke na wanke Zimmerman daga laifin aikata kisa.

Mawallafiya. Halima Balaraba Abbas
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe