1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jerin tashin bama-bamai a Abuja

Usman Shehu UsmanOctober 3, 2015

Akalla mutane 15 suka mutu wasu kimanin 40 suka jikkata bayan tashin bama-bamai a Kuje da Nyanya, wadanda anguwanni ne a babban birnin Tarayyar Najeriya.

Anschlag in Nigera
Hoto: dpa

Rahotanni sun bayyana cewa bama–bamai biyu ne suka tashi a cikin garin Kuje, shelkwatar karamar hukumar Kuje a babban birnin Tarayyar Najeriya. Alhaji Shuaibu Mai Tifa mazaunin Kuje ya yi wa DW karin bayani, inda ya ce hari daya an kai shi ne a harabar ofishin 'yan sanda, yayin da daya harin aka kai shi a kasuwar garin wanda kuma wata mahadar hanya ce da ke da cunkoson jama’a. Ana tsoron mutane da dama sun mutu a harin.

A anguwar Nyanya ma wani bam din ya tashi, inda ya fashe a karkashin wata gada da aka taba tada wani bam din a Abuja. An fuskanci fashewar bama-baman ne kwana guda bayan bikin cikar Najeriya shekaru 55 da samun ‘yancinta. Kuma kusan mazauna a Abuja har sun saki jiki sun manta da ganin irin wannan tarzoma sama da shekara guda.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW