Jirgin Lufthansa ya yi saukar gaggawa a Masar
March 6, 2026
Wani jirgin saman Lufthansa da ya tashi daga birnin Munich na Jamus zuwa Riyadh na Saudiyya ya yi saukar gaggawa a birnin Alkahiran Masar a yau Juma'a saboda dalilai na tsaro sakamakon rikicin da ke faruwa a Gabas ta Tsakiya.
Babban jami'in kamfanin Lufthansa, Carsten Spohr, ya ce matuƙin jirgin ne ya yanke shawarar karkatar da shi zuwa Alkahira bayan ya tattauna da hedikwatar kamfanin da ke Frankfurt.
Barazanar yajin aiki a kamfanin jiragen saman Lufthansa
Ya ce, “tsaro shi ne abu na farko muhimmi da ya kamata a mayar wa hankali musamman a irin wannan lokacin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya."
A cewar Lufthansa, filin jirgin saman babban birnin Saudiyya, wato Riyadh, ya kasance a rufe a lokacin da jirgin ke shirin sauka.
Kamfanin jiragen sama na Lufthansa zai rage ma'aikata 4,000
Kamfanin ya ce har yanzu jirgin na Lufthansa da zai taso daga Saudiyya wanda tuni ya cika da fasinjoji bai taso ba tukunna