Joseph Kony ya aikata mummunar ta'asa
May 21, 2013
Talla
A cikin wani rahoton da hukumar ta Majalisar Ɗikin Duniyar da ke kare hakin bil addama ta wallafa tun a shekarun 1997 wanda za ta bayyana a nan gaba.
Ta ce haka gugun mayaƙan da Kony ke yiwa jagora ana tuhumar su da laifin sace yara ƙanana kimanin dubu 60 zuwa dubu 100. Waɗanda su suke sakawa cikin aikin soji, duk da ma cewar shekarun su, ba su kai ba. Tare da tilatawa wasu mutane miliyan biyu da rabi barin gidajensu.
Ƙungiyar dai ta LRA wace ke ɗaya daga cikin ƙungiyoyijn da ke yin yaƙin sari ka noƙe tun a shekarun 1988 a yankin arewacin ƙasar Yuganda. Yanzu haka mayaƙanta sun bazu zuwa a yanki arewa maso gabshin Kwango da Afirka ta Tasakiya da kuma Sudan ta Kudu.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman