Kamaru: An kashe sojojin gwamnati
December 19, 2017Talla
Hukumomin gwamnati a Kamaru sun ce dakarun gwamnatin sun kashe wasu daga cikin 'yan awaren kasar bayan da sabon rikin ya barke, sai dai basu bayyana adadin wadanda aka kashe ba kawo yanzu.
Shugaban 'yan awaren da ke son kafa yankin Ambazoniya John Fru Ndi, ya caccaki gwamnati na rashin daukar matakan da suka dace a duk lokacin da aka samu kunnowar rikicin a yankin.
Jami'an tsaro sun kashe mutane da dama tun bayan da aka fara zanga-zangar neman kafa yanki mai cin gashin kai a Kamaru, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce akwai 'yan yankin 40,000 da ke gudun hijira a makwabciyar kasar Najeriya.