SiyasaAfirka
Kano na jimamin mutuwar 'yan majalisa 2 a rana daya
December 24, 2025
Talla
Dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Ungoggo kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar, Hon Aminu Sa'adu Ungoggo, ya rasu ne bayan da ya yanke jiki ya fadi jim kadan bayan isa harabar majalisar. An garzaya da shi asibiti, amma daga bisani likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Awa guda bayan sanar da rasuwar Hon. Aminu Ungoggo, sai kuma aka samu labarin rasuwar wani dan majalisar dokokin jihar, Hon Sarki Aliyu Daneji, mai wakiltar karamar hukumar Birnin Kano da Kewaye.
Kawo yanzu dai jihar Kano na cikin jimami da alhini, yayin da jama'a da dama ke bayyana mamaki da alhinin rasuwar yan majalisun biyu a rana guda.