Burkina da Mali za su karfafa matakan tsaron iyakokinsu
August 27, 2019![Burkina Faso Sicherheitskräfte](https://static.dw.com/image/48527878_800.webp)
Talla
A yayin da yake ganawa da firaministan Burkina Faso Christophe Dabiré a yammacin jiya, ministan tsaron Mali Janar Ibrahima Dembélé, ya ce tuni bangarorin kasashen biyu suka fara kaddamar da tsaron iyakokinsu na hadin gwiwa, a wani yunkuri na kawo karshen hare-haren ta'addancin da ke addabar kasashen biyu da kuma suka yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.