1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar Libiya ta fada cikin rikicin siyasa

January 22, 2012

A wani lamarin koma baya ga farfadowar kasar daga yakin basasa, mataimakin shugaban gwamnatin Libiya Abdul-Hafiz Ghoga ya ajiye aikinsa

Libyans damage the car of National Transitional Council (NTC) Chairman Mustafa Abdel Jalil, to express their dissatisfaction towards the policy of the Council in governing the country, in Benghazi January 21, 2012. People in Benghazi, birthplace of the revolt which forced out former Libyan leader Muammar Gaddafi, have been protesting for weeks to demand the sacking of Gaddafi-era officials and more transparency about how the NTC is spending Libyan assets. REUTERS/Esam Al-Fetori (LIBYA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST)
Masu boren adawa da sabbin mahukunta Libiya a birnin BenghaziHoto: Reuters

Mataimakin shugaban gwamnatin rikon kwarya a Libiya Abdul Hafiz Ghoga ya yi murabus. Ghoga yace ya ajiye aikinsa ne bisa jerin zanga-zanga da aka yi ta gudanarwa a kasar, abinda kuma kamar yadda ya kwatata da cewa ba zai yi wa kasar alheri ba. Boren da ake yi dai ya girgiza gwamnatin rikon kwarya, abinda ya sa ake gudun rugujewar al'amura a kasar, wanda ke farfadowa tun bayan farmakin da yakin basa da kuma hare-haren jiragen yaki na kasashen kungiyar tsaro ta NATO, wadanda suka kai ga kisa da kuma kifar da gwamnatin Muammar Gaddafi. A yammacin jiya matasa da suka fusata a birnin Benghazi sun kutsa kai cikin ginin gwamnati a dai-dai lokacin da babban jami'i mafi girma a birnin ke cikin ofishin, inda suke bukatar sai gwamnatin rikon kwaryar wanda aka sani da NTC ta yi murabus.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu