1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen Larabawa na nazarin alakarsu da Isra'ila

September 16, 2025

Shugabannin kasashen Larabawa da na Musulmi, sun yi kiran da a sake duba dangantakar da ke tsakaninsu da kasar Isra'ila, bayan harin da kasar ta kai kasar Qatar cikin makon jiya.

Doha 2025 | Taron gaggawa na Larabawa da Musulmai kan harin Isra’ila a kan Qatar
Doha 2025 | Taron gaggawa na Larabawa da Musulmai kan harin Isra’ila a kan QatarHoto: Mahmud Hams/AFP

Wannan kiran ya fito ne cikin sanarwar haɗin gwiwa ta shugabannin ƙasashe kusan 60, mambobin kungiyar Ƙasashen Larabawa da ta Musulmin, bayan taron gaggawa da suka gudanar a ranar Litinin a birnin Doha na kasar Qatar.

Shugabannin sun bayyana cewa, baya ga tunanin sake fasalin huldar diflomasiyya da Isra’ila, dukkanin kasashen mambobi kamata ya yi su dauki matakan shari’a da na aiki tare don dakile Isra’ila daga ci gaba da kai hare-hare a kan Falasdinawa.

Harin Isra'ila a Doha ya tarwatsa kokarin diflomasiyyar da Qatar da Masar suka jagoranta domin kawo karshen yakin da ya dauki kusan shekaru biyu a Zirin Gaza