1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Kasashen Larabawa sun bukaci a kawo karshen yakin Gaza

May 16, 2024

Kasashen Larabawa sun kammala taro a birnin Manama na kasar Baharein inda suka bukaci Majalisar Dinkin Duniya ta dauki mataki na kawo karshen yakin Gaza da ke ci gaba da lakume rayukan Falasdinawa.

Kasashen Larabawa sun bukaci a kawo karshen yakin Gaza
Kasashen Larabawa sun bukaci a kawo karshen yakin GazaHoto: Qatar Amiri Diwan/Handout/Anadolu/picture alliance

Kungiyar kasashen Larabawa ta bukaci da a kai jami'an wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dindin Duniya zuwa yankunan Falasdinawa da Isra'ila ta mamaye, kafin a cimma daidaito na kafa kasar Falasdinu mai cikakken 'yanci.

Sai dai da akwai wuya wannan kira ya yi tasiri, duba da sarkakiyar rikicin da aka share shekaru ana yi a wannan yanki.

Karin bayani: G20 ta amince da samar da kasar Falasdinu

A cikin sanarwar da ta biyo bayan taron da aka kammala a ranar Alhamis, shugabannin kasashen Larabawan sun bukaci a shirya babbar mahawara ta kasa da kasa a karkashin inuwar Majalisar Dindin Duniya domin kawo karshen zubar da jini a zirin Gaza da yaki ya daidaita.

Karin bayani: Majalisar Dinkin Duniya ta ce samar da kasar Falasdinu ya zama wajibi

Sai dai girke jami'an wanzar da zaman lafiya na MDD a yankin Falasdinu abu ne da ke bukatar samun sahalewa daga Isra'ila, abinda wasu masana ke ganin cewa zai yi matukar wahala ko ma ba zai yiwu ba.

A daya bangaren kuma firaministan Isra'ila Benjamin Netenyahu ya kasance babban mai adawa da matakin kafa kasar Falasdinu mai cikakken 'yanci a matsayin mafita ga rikicin yankin, duk da karbuwa da wannan shawara ke samu a gurin Amurka da wasu kasashen nahiyar Turai.