1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kasashen Sahel biyar na atisayen soji a Jamhuriyar Nijar

May 26, 2024

Ma'aikatar tsaron Jamhuriyar Nijar ta ce kasashen yankin Sahel biyar na gudanar da atisayen soja irinsa na farko a yammacin kasar, da ke fama da ayyukan masu ikirarin jihadi da ke dauke da makamai.

Sojojin Burkina Faso da na Niger a lokacin da suka karbar horon hadin gwiwa daga sojojin Amurka
Sojojin Burkina Faso da na Niger a lokacin da suka karbar horon hadin gwiwa daga sojojin AmurkaHoto: Issouf Sanogo/AFP

Nijar wacce ke karbar bakuncin itisayen a yankin Tillaa, ta ce kasashen yankin Sahel din da suka shiga shirin sun hada da Burkina Faso da Chad da Mali da Togo sai kuma Nijar mai masaukin baki.

Karin bayani: Sojoji sun tsawaita wa'adin mulkinsu a Burkina Faso 

Uku daga cikin kasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Mali da suka hambarar da gwamnatocin farar hula sun fatattaki dakarun Faransa da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasashen, da zummar ci gaba da daukar ragamar yaki da 'yan ta'adda a shiyyar tare da maida hankali kan neman goyon bayan kasar Rasha.

Karin bayani: Chadi da Mauritaniya sun amince da rusa G5 Sahel

Kutsen sojoji a gwamnatocin kasashen ya sake haifar da matsalar tsaro da rudanin siyasa da bukatar kayan agajin jinkai a kasashen uku.