Za a bude iyakokin cikin gida na Turai
June 15, 2020![Brüssel EU Coronavirus Luftbrücke Demokratische Republik Kongo](https://static.dw.com/image/53735326_800.webp)
A wannan Litinin da yawa daga cikin kasashen Turai na kungiyar EU ke bude kan iyakokinsu watanni da dama bayan rufe su saboda cutar COVID-19.
Sai dai akwai bukatar ko da an bude iyakokin mutane kar su yi nisa da kasashensu a wani mataki na farfado da tattalin arzikin kasashen musamman a fannin yawon bude ido.
Faransa da ke zama kasa ta farko a wannan fanni na kira ga al'ummar ta da su yi hutunsu na rani a cikin kasar maimakon kai kudadensu wasu kasashen. A yayin da a hannu guda suke shirin fara wani shiri mai taken "A Faransa zan yi hutun rani na"
Kasar Spain ta sanar da cewar ba za ta bude iyakokinta a wannan rana ba a yayin da ta ke shirin karshe na karkabe cutar COVID-19. Birtaniya wacce dama bata rufe nata iyakokin ba bata cikin wannan shirin sai dai ta ce duk mai shiga kasarta sai ya yi makwanni biyu a kebe.