1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Katsewar hulɗar Iran da Holland

January 30, 2011

Ƙasar Holland ta katse hulɗa tsakanita da Iran bisa hukuncin kisa da Iran ɗin ta zartar akan wata mata 'yar asalinta mai riƙe da fasfo na Holland.

Alamar shari'a a IranHoto: FARS

Gwamnatin ƙasar Holland ta katse hulɗa tsakaninta da Iran bayan da jamhuriyar ta Islama ta zartar da hukuncin kisa ga wata mata 'yan asalinta mai riƙe da fasfo na Holland bisa laifin fataucin fodar iblis wato cocaine zuwa wannan ƙasa . Ministan harkokin wajen Holland, Uri Roesental ya kira zartar da hukuncin kisa akan Zahra Bahrami mai shekaru 46 da haifuwa tamkar ɗanya da azzaluman gwamnati ta aikata. Bahrami dai na daga cikin waɗanda suka bayyanar ga kyamarsu ga gwamnatin Iran. A shekarar 2009 ne aka kame ta bayan da ta shiga zanga-zangar nuna adawa da sake zaɓar Shugaba Mahmud Ahmadnejad .

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Usman Shehu Usman