1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka na fuskantar matsin lamba kan kisan Khashoggi

Zulaiha Abubakar
November 18, 2018

Fadar mulkin Amirka ta baiyana cewar nan gaba kadan za ta baiyana matsayarta kan sakamakon rahoton hukumar leken asirin kasar game da kisan dan jarida Jamal Khashoggi.

USA Trump besucht Brandgebiete in Kalifornien
Hoto: picture-alliance/dpa/E. Vucci

A baya dai Saudiyya ta yi amai ta lashe game da wannan batu kafin a farkon wannan mako a jiyo maigabatar da kara masarautar na kokarin wanke Yarima Mohammed bin Salman kan wannan batu.

Kisan Jamal Khashaoggi mai shekaru 58 a karamin ofishin Saudiya da ke birnin Santanbul na kasar Turkiyya na zaman kalubale ga cigaban kawance tsakanin Amirka da kasar ta Saudiyya.