1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Khashoggi: Jamus ta kira jakadan Saudiyya a Berlin

October 22, 2018

Hukumomin kasar Jamus sun bukaci bahasi daga jakadan Saudiyya dangane da kisan Jamal Khashoggi dan jaridan nan dan kasar Saudiyya.

Jamal Khashoggi
Hoto: picture-alliance/AP Photo/V. Mayo

Ma'aikatar harkokin wajen Jamus ce ta gayyaci jakadan Saudiyya da ke kasar, don tattauna batun da ke daukar hankali a duniya, wato kisan da aka yi wa dan jaridan Jamal Khashoggi.

Mai magana da yawun ma'aikatar Maria Adebahr, ta ce ganawar ce za ta tabbatar da matsayin gwamnatin Jamus kan batun mai matukar takaici.

A jiya Lahadi ne kuwa shugabar gwamnati Angela Merkel, ta bayyana cewa Jamus ta dakatar da sayar wa da Saudiyya da makamai.

Shugaba Erdogan na urkiyya dai ya yi alkawarin bayyana abin da ya faru dalla-dalla ga duniya, a ranar Talata.