1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Ko alaka za ta inganta da Benin?

Salissou Boukari LMJ
April 24, 2026

Tun bayan zaben da aka yi a kasar Benin da ya bayar da damar samun sabon shugaban kasa, al'ummar Jamhuriyar Nijar ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan matakin farfado da hulda tsakanin kasashen biyu.

Benin | Shugaban Kasa | Romuald Wadagni
Sabon shugaban kasar Benin Romuald WadagniHoto: Ute Grabowsky/BMZ/photothek.de/picture alliance

Zababben shugaban kasar ta Benin dai ya yi wasu kalaman cewa, abin da ya fi shi ne a fuskanci juna domin rashin yin hakan ba zai magance matsaloli ba. A nasu bangaren hukumomin Jamhuriyar Nijar na ganin babbar matsalarsu da Benin ita ce, kasancewar sojojin Faransa. Koda yake wasu na ganin cewa Benin kasa ce mai 'yanci da ke iya hulda da wanda taga dama.

Yiwuwar cikar burin al'umma?

Abubuwa Biyar tare da Sedik Abba

04:20

This browser does not support the video element.

Tun dai farkon wannan matsala kungiyoyin fararan hula kamar FCR da Oumarou Souley ke jagoranta, sun sha jaddada kiransu ga bangarorin biyu kan su dubi al'umma su daidata hulda a tsakaninsu. A cewarsa, a yanzu idan har Benin ta bayar da tabbaci ga Nijar ya kamata ita ma Nijar ta duba lamarin. Masu iya magana dai na cewa, mai daki shi ya san inda yake masa yoyo.

Wahalhalu ga mazauna kan iyaka

A shirye Najeriya take ta kare dimokuradiyya

01:32

This browser does not support the video element.

Ga mutanen da ke rayuwa a kusa da iyakokin kasashen Nijar da Benin da Nijar da Najeriya, su kadai suka san halin da suke ciki. Masana na da ra'ayin cewa abun jira a gani dai shi ne, matakin da Sabon shugaban na Benin Wadagni zai dauka, na ganin ya shirya da makwabtansa na yankin Sahel da su kansu makwabtan nasa ya kamata su yi don lamura su daidaita al'umomi su samu sassauci na rayuwa.

Gyarawa da wallafawa: Lateefa Mustapha Ja'afar

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani