1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamhuriyar Nijar: Ina makomar ilimi?

Salissou Boukari
June 3, 2025

Babbar kungiyar dalibai da 'yan makaranta ta kasa a Nijar USN, ta yi gargadi kan fargabar kama hanyar tabarbarewar ilimi saboda rashin daidaito tsakanin gwamnati da malaman makaranta.

Nijar | Mafita | Makarantu | Ilimi
Neman kawo gyar ga makarantu a Jamhuriyar NijarHoto: Gazali Abdou/DW

Cikin wata sanarwar da babbar kungiyar dalibai ta kasa ta Nijar din ta fitar, ta ce yanayin da aka shiga na kafewa kan baka ba tare da fuskantar juna domin nazarin matsalolin ba na saka tsarin karatu cikin halin rashin tabbas musamman ma a wannan lokaci da ake shirin fara jarabarawar karshen shekara. A dangane da haka ne kungiyar ta USN ta yi kira ga ofishin ministan ilimi da horo na kasa da ya dubi girman wannan matsala, domin samar da kyakkyawar mafita. Cikin sanarwar kungiyar daliban ta yi tir da yanayin da aka shiga, inda makarantun gwamnati kusan suka tsaya cak yayin da masu zaman kansu ke aiki.

Nijar: Matsalar tsaro ta shafi ilimi

04:01

This browser does not support the video element.

Tuni dai shugabannin kungiyar iyayen 'yan makaranta suka ce suna ciki tattaunawa da bangarorin, domin samun mafita. Sai dai Honorable Alhaji Mouazou Tchagalla tsohon dan majalisar dokoki kuma uba ya ce, batun ilimi na yara wanda sune manyan gobe wajibi ne kuma bai kamata a yi ja-in-ja a kani ba.  An dai jima ana fama kan wanan batu na magance matsalar kwantaragi a fannin ayyukan malaman makaranta a Nijar, inda aka sha zama tsakanin gwamnati da kungiyoyin malaman domin samun jituwa a fannin daukar malamai a matsayin ma'aikatan din-din-din.

Nijar: Kasuwar littafan kan titi na bunkasa

03:54

This browser does not support the video element.

Acewar Kassoum Issa tsohon magatakarda na babbar kungiyar Malaman Makaranta ta kasa, lokaci ya yi da ya kamata a dauki matakan gyara. Kungiyar dalibai da 'yan makaranta na kasa baki daya dai ta yi kira ga magoya bayanta 'yan makaranta da su hada kai, domin ganin sun fuskanci wannan matsala da kuma kwato hakkokinsu na samun karatu yadda za su samu kyakkyawar makoma.