SiyasaIran
Iran: Ko Tehran na bunkasa nukiliyarta?
September 17, 2025
Talla
Ministan harkokin kasashen waje na Iran din Abbas Araghchi ne ya bayyana hakan, jim kadan bayan tattaunawar da suka yi da takwarorinsa na Birtaniya da Faransa da Jamus da ake wa lakabi da kasashen E3 da kuma jami'ar hulda da kasashen ketare ta kungiyar EU ta wayar tarho. Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta cimma matsayar da za ta yi wa kowa dadi, sai dai ya ce kai wa ga hakan na bukatar taka-tsan-tsan wajen tunkarar lamarin daga kasashen Turan uku.