1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso: Sabon matakin kan batun tsaro?

Philipp Sandner MAB/LMJ
April 30, 2026

Yanayin tsaro na ci gaba da tabarbarewa a yankin Sahel duk da matakan hadin gwiwa da gwamnatocin kasashen ke ikirarin dauka, amma bayan harin da aka kai kwanan nan a Mali makwabciyarta Burkina Faso na dada daura damara.

Bukina Faso | Gwamnatin Soja | Tsaro | Kyaftin Ibrahim Traoré
Shugaban kasar Burkina Faso Kyaftin Ibrahim TraoréHoto: Stanislav Krasilnikov/RIA Novosti/Anadolu/picture alliance

Muhimmin aiki ne da gwamnatin mulkin sojan ta Burkina Faso ta sa a gaba, kafin karshen shekara tana da niyyar horar da dakarun ko ta-kwana guda 100,000. Majalisar ministoci ta wannan kasa da ke  yankin Sahel ce ta amince da wannan daftarin doka, a wani mataki na karfafa tsarin tsaron kasar. A halin yanzu dai, rundunar sojojin Burkina Faso ta kunshi kusan jami'a 12,000. Wannan yana nufin cewar adadin sababbin dakarun ko ta-kwana zai ninka yawan sojojin kasar sau takwas. Bisa ga wannan tsarin za a fifita daukar ma'aikata da suke da kwarewa a fannin tsaro, yayin da za a bai wa sauran cikakken horo.

Mataki mai kyau, amma akwai sauran rina......

Léboure Crépin Zanzé kwararre kan tsaro a Dakar na Senegal ya ce, manufa ce mai kyau domin gwamnati na son aikawa da sako mai karfi. Amma ana bukatar jerin abubuwa, domin cimma nasarar samar da dakarun ko ta-kwana. Burkina Faso ta kasance karkashin jagorancin mulkin soja tun 2022, kuma gwamnatin da Kyaftain Ibrahim Traoré ke jagoranta ta yi alkawarin samar da tsaro sakamakon barazanar ta'addanci da take fuskanta. Sai dai har yanzu, ba a samu wani ci-gaban a zo a gani a wannan fannin ba. Masharhanta sun nunar da cewa, kusan kaso 60 cikin 100 na Burkina Faso ba ya karkashin ikon hukuma. Maimakon haka ma, kungiyoyin da ke da tsaurin kishin Islama kamar JNIM da sauran su na yawan kai hare-hare a kan sansanonin sojoji.

Hira da ministan harkokin wajen Najeriya

03:43

This browser does not support the video element.

Hasali ma, duk kanwar ja ce a kasashen da ke cikin kawance AES kamar Mali da Nijar. Ko da a karshen makon da ya gabata, masu tsattsauran ra'ayi sun kai hare-hare a wurare dabam-dabam a fadin kasar Mali. Wannan dai ya raunana matsayi da kimar Rasha da ke kawance da kasashen Sahel, saboda an yi tsammanin za ta taimaka wajen tabbatar da tsaro a dukkan kasashen Sahel guda uku. Beverly Ochieng mai sharhi a Cibiyar Tuntuba ta Control Risks ta ce, Burkina Faso na son nuna za ta iya cimma nasara a fannin tsaro ba tare da taimakon tsofaffin abokan huldarta kamar Faransa ba.

Mataki cikin taka tsan-tsan

Amma ta ce sakamakon matsin lamba da take fuskanta a cikin da wajen kasar, ya zama wajibi ta yi sara tana mai duban bakin gatari. Sai dai diban dakarun ko ta-kwana na iya haddasa kalubalen tsarin bin umarni na soja, sakamakon rundunoni dabam-dabam da za a samu. Sannan za a iya samun rashin daidaito a tsakanin rundunoni lamarin da ka iya haifar da cin-zarafi, in ji kungiyoyin kare hakkin dan Adam na Burkina Faso.

Translated by Mouhamadou Awal Balarabe

Edited and Published by Lateefa Mustapha Ja'afar

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani