Koma baya a yunkurin sulhunta rikicin Siriya
November 27, 2017![Kasachstan Astana Syrien Gespräche](https://static.dw.com/image/40532153_800.webp)
Batun tattaunawar ta wanzar da zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ke jagoranta ya fuskanci tarnaki biyo bayan bukatar ganin lallai sai shugaba Bashar al-Assad ya sauka daga karagar mulkin kasar, a yayin da gwamnatin Assad din ke ikirarin samun nasara a sake karbe ikon wasu yankunan kasar daga hannun 'yan tawaye.
A wani rahoto da wata jaridar kasar ta wallafa a wannan Litinin, ta ce wakilan gwamnati ba za su sami damar hallarta zaman sulhunta rikicin a gobe Talata kamar yadda aka tsara ba, sabili da matakin kungiyar hadaka da tace a fitar da shugaban daga lissafin kowacce gwamnatin rikon kwarya da za a kafa nan gaba in har an kai ga cimma yarjejeniya a taron na Geneva. Gwamnatin Siriya a na ta bangaren ta ce taron zai iya yin tasiri in har 'yan tawaye sun bi umarninta na ajiye makamai. Daruruwan mutane ne suka rasa rayukansu tun barkewar yakin basasa a Siriya lamarin da aka ce ya haifar da matsalar 'yan gudun hijra mafi muni a tarihi.