Gwajin makami a Koriya ta Arewa
May 25, 2022![Makamin Nukiliya | Koriya ta Arewa](https://static.dw.com/image/61041247_800.webp)
Talla
Tuni dai mahukuntan Seoul suka nuna damuwarsu, inda majalisar tsaron kasar ta yi wani taro domin tattauna lamarin. A nasa bangaren ministan tsaron kasar Japan, Nobuo Kishi ya bayyana gwajin makamai masu linzamin na Koriya ta Arewa da neman tayar da zaune tsaye, wanda kuma ya ce ba za a lamunta ba. Koriya ta Arewa dai na fama da tarin takunkumai sanadiyyar shirinta na makaman nukiliya, sai dai a mahukuntan Pyongyang din na nuna halin ko in kula dangane da takunkuman.