Kotu ta umurci ASUU da ta koma bakin aiki
September 21, 2022![Nigeria Bayero Universität in Kano](https://static.dw.com/image/18399114_800.webp)
Talla
Mai shari'a Polycarp Hamman ya bukaci malaman jami'o'in su koma bakin aiki zuwa nan da dan lokacin da zai yanke hukunci a kan shari'ar da mahukuntan Najeriyar suka shigar da kara a gaban shi.
Sama da watanni 7 ke nan da aka rufe jami'o'i a Najeriya bisa neman karin albashi da kuma wasu alawus-alawus da malaman suka nema daga gwamnatin tarayya.
Wannan matakin na kotu dai na zuwa ne bayan da a jiya dali'bai a wasu sasan kasar suka gudanar da zanga-zangar neman a bude makarantu domin ci gaba da daukar darussa.