Kotun duniya ICC ta dakatar da binciken rikicin Kenya
November 28, 2023![](https://static.dw.com/image/66258730_800.webp)
Kotun hukunta masu aikata manyan laifuka ta duniya ICC da ke Hague ta dakatar da binciken da ta shafe sama da shekaru 13 tana gudanarwa a kan mummunan tashin hankalin da ya janyo mutuwar mutane sama da dubu guda a kasar Kenya, bayan zaben shugaban kasa na shekarar 2007.
Karin bayani:Ambaliya ta kashe mutane 70 a Kenya
Masu gabatar da karar sun sanar da dakatar da binciken ne a Litinin din nan, inda kuma suka bukaci karin kudaden gudanarwa don ci gaba da bincike kan rikicin Rasha da Ukraine da kuma na Isra'ila da kungiyar Hamas.
Karin bayani:Sarki Charles na Ingila na ziyara a Kenya
Daga cikin wadanda aka tuhuma da hannun a tashin hankalin na Kenya har da tsohon shugaban kasar Uhuru Kenyatta da mataimakinsa na lokacin kuma shugaba a yanzu William Ruto.