Kotun ECOWAS ta ce gwamnatin Najeriya ke laifi
December 17, 2012Ƙungiyoyin kare haƙƙin jama'a sun jinjinawa hukuncin da kotun al'ummar yankin Afrika ta yamma wato ECOWAS ta yanke, inda ta umurci gwamnatin Najeriya da ta tilastawa hukunta kamfanonin man da suke gurbata muhalli a yankin Niger Delta mai arzikin mai a kasar.
Wannan hukunci da ake wa kallo mai cike da tarihi a fafutukar da aka dade ana ci gaba da yi don shawo kan matsalolin gurbata muhalli a yankin Niger Delta mai afrzikin man fetur, wanda matsalolin gurbacewar muhalli ke ci gaba da jefa rayuwar al'ummar yankin cikin mawuyacin hali.
Kotun ta Ecowas da hakkake cewar gwamnatin Najeriyar ta karya dokar kuduri ta 21 na yancin rayuwan kasashen Afrika da kuma kuduri na 24, bisa gazawarta wajen kare al'ummun yankin Niger Delta daga ayyukan kamfanonin mai da suka gurbata masu muhallin. To ko wace hanya wannan ya shafi batun take hakkin jama'a da masu fafutuka a wannan fannin ke danganata shi da gurbata muhallin? Malam Alhassan Mahmoud na kungiyar kare hakin jama'a da tsaron kasa na cikin masu fafutuka a kan wannan lamari.
"Wannan hukunci da kotun ECOWAS ta yi abinda ya nuna shine akwai abubuwan da ya kamata a yi wa bil-Adama da ba'a yi ba. Ba ma a yankin Niger Delta kadai ba don abin da ya sa duniya ta san nasu don suna da mai ne da ake samun malalewarsa, to don haka akwai sauran wurare a Najeriya da ake fama da wannan matsala kaman in ka duba misali Kainji inda ake samar da wutar lantarki ba wai ga Najeriya kadai ba"
Batun gurɓacewar muhalli da ake zargin kamfanonin da ke hako mai a yankin Niger Delta dai lamari ne da aka dade ana ja in ja a kansa musamman ganin lamari ne da kwararru suka bayyana illarsa ga rayuwar alummar yankin saboda yadda yake gurbata ruwa, iska da ma kasar noman da suka dogara a kanta.
Tuni wannan ya haifara da tada jijiyar wuya a tsakanin alummun yankin da ma kungiyoyin kare hakkin jama na cikin Najeriyar da kasashen ketare abinda ya sanya Chief Asara Sinos na yankin Niger Delta da ke cikin wadanda suke fafutukar wanna lamari bayyana cewa.
Yace "abinda muke cewa shine gwamnati ta bamu muhallinmu ta gyara shi ya kasance mai tsafta, amma in gwamnati na ci gaba da nuna rashin kulawa to ba za mu lamunci hakan ba"
An daɗe ana kokarin tankwasa gwamnatin Najeriyar ta dauki mataki a kan irin wadannan laifuffuka na gurbata muhalli ba tare da samun wani ci gaba.
Domin har zuwa wannan lokaci ana ci gaba da jan in ja a tsakanin gwamnatin Najeriya da kamfanion Shell a game da aikin share gurbataccen man da ya malala a yankin Ogoni na Niger Delta.
Abin jira a ganin shine matakin da gwamnatin Najeriyar za ta dauka a kan wannan hukunci na kotun ta ECOWAS.
Mawallafi: Uwaisu Abubakar Idris
Edita: Usman Shehu Usman