1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun ECOWAS ta yi umarni a saki Bazoum

Uwais Abubakar Idris
December 16, 2023

Kotun Ecowas ta yanke hukuncin cewa gwamnatin mulkin soji ta Jamhuriyar Nijar ta take hakkin shugaban kasar da aka yi wa juyin mulki Bazoum Mohammed don haka ta bukaci sun hazarta sakinsa ba tare da jinkiri ba

Deutschland l Besuch des Nigerianischen Präsidenten in Berlin
Hoto: Presse- und Kommunikationsdienst der Präsidentschaft von Niger

Kotun ta bayyana dokoki tsarin mulkin kungiyar ta ECOWAS da kudirorin Majalisar Dinkin Duniya da duka suka nuna babban laifi ne a tsare mutum ba tare da tuhuma kan laifin da ake zarginsa da aikatawa ba.

Da yake yanke hukunci, mai shari'a Gbéri-Bè Ouattara ya bayyana cewa kowane dan Adama yana da iko ya wala a ko ina. Don haka sojojin sun tafka laifi da suke ci gaba da tsare Mohamed Bazoum. Lauyoyin da suka shigar da karar a madadinsa sun saurari hukuncin ne ta kafar sadarwa ta Internet. Tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar suke tsare da Bazoum Mohamed. 

Karin Bayani:ECOWAS na kan bakanta a kan Nijar

Hukuncin kotun dai muhimmin ci gaba ne ga kungiyoyin da ke fafutukar kare hakin jama'a a Afrika da ma sauran sassan duniya. 

A shari'ar da kotun kolin Najeriya ta yanke a kan karar da shugaban haramtaciyyar kungiyar IPOB  Nnamdi Kanu ya shigar gabanta, Kotun ta jingine hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke cewa baya da laifin ta'adanci a kansa. Kotun kolin ta ce za'a ci gaba da shari'ar sa a kotu a saboda haka babu batun a sake shi.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani