Kotun ECOWAS za ta yanke hukunci kan makomar takarar Sonko
November 6, 2023![Senegal Oppositionsführer Ousmane Sonko](https://static.dw.com/image/66381766_800.webp)
Lauyoyin da ke kare dan adawan da ya shiga takun saka da gwamnatin Macky Sall ne suka shigar da kara a gaban kotun mai ofishi a birnin Abuja na Najeriya domin neman a wankesa daga tuhume-tuhume da ake yi masa, wadanda ka iya hana masa tsayawa takara.
Karin bayani:An tsare madugun adawar Senegal Ousmane Sonko a gidan yari
Dama dai a ranar 12 ga watan Oktoba da ya gabata wani alkali a birnin Ziguinchor da ke Kudancin Senegal ya soke matakin hanawa Ousman Sonko tsayawa takara a zaban shugaban kasar da za a gudanar a ranar 25 ga watan Fabaru na shekarar 2024 mai kamawa.
Karin bayani: Jagoran adawar Senegal na sake yajin cin abinci
Wannan dambarwa dai na zuwa ne yayin da ya rage makwanni uku kacal a rufe karbar takardun takarar shugabancin kasa, to sai dai lauyoyin da ke kare Sonko mai shekaru 49 da haihuwa sun ce ya zama wajibi a gaggauta zartar da hukuncin da alkalin Ziguichor ya yanke don kadda loakaci ya kure.