1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Kotun Iran ta janye hukuncin kisa da aka yanke wa mawaki

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
June 22, 2024

An dai kama mawakin mai shekaru 33 a cikin watan Oktoban shekarar 2022, bayan kazamar zanga-zangar da ta biyo bayan mutuwar matashiyar, wadda aka kama bisa laifin rashin yin lullubi

Hoto: Claire Serie/BePress/ABACA/picture alliance

Kotun kolin Iran ta janye hukuncin kisan da aka yanke wa fitaccen mawakin kasar Toomaj Salehi, wanda aka daure bayan samunsa da laifin tunzura jama'a gudanar da zanga-zanga sakamakon mutuwar matashiya Mahsa Amini a hannun jami'an tsaron kasar.

Karin bayani:Iran: Shekara guda da mutuwar Jina Amini

Lauyansa Amir Raisian ne ya wallafa janye hukuncin a shafinsa na X, yana mai cewa kotun kolin ta bada umarnin sake nazartar shari'ar, sakamakon kurakuran da ta ce an tafka a shari'ar, bayan tun da farko an yanke masa hukuncin kisan a cikin watan Afirilun da ya gabata.

Karin bayani:Iran ta aiwatar da hukuncin kisa kan wasu mutum uku

An dai kama mawakin mai shekaru 33 a cikin watan Oktoban shekarar 2022, bayan kazamar zanga-zangar da ta biyo bayan mutuwar matashiyar, wadda aka kama bisa laifin rashin yin lullubi.

Zanga-zangar dai ta janyo mutuwar darurun Iraniyawa ciki har da 'yan sanda.