Kwale-kwale ya kife da 'yan ci rani 46
June 7, 2018![Jemen Migranten](https://static.dw.com/image/44104733_800.webp)
Talla
Wadanda suka tsira daga hatsarin sun ce lamarin ya faru ne sakamakon rashin sanya rigunan kariya. Masu ayyukan ceto sun ce kwale-kwalen na dauke da kusan 'yan ci rani 100, wandanda suka tashi daga tashar jirgin ruwa ta Bosaso a Somaliya da nufin Zuwa kasar Yemen neman aiki.
Hukumar kula da kauran jama'a ta duniya IOM ta ce a karshen makon da ya gabata wasu mutane 112 sun mutu bayan da kwale-kwale ya kife da su a Tekun Tunisiya.