1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gasar Olympics cikin Labarin Wasanni

Suleiman Babayo LMJ
July 22, 2024

Shirye-shiryen fara wasannin guje-guje da tsalle-tsalle na duniya nan da kwanaki a birnin Paris na kasar Faransa.

Tour de France 2024 | Tadej Pogacar | Tagwayen Kambu
Zakaran tseren keke na tagwayen kambu Tadej PogacarHoto: Manon Cruz/REUTERS

Tadej Pogacar ya zama dan tseren keke na farko da ya lashe tagwayen kambu na Giro d'Italia/Tour de France double, tun bayan shekara ta 1998. Dan kasar Soleveniya da ya lashe kambunsa na uku a Lahadin karshen mako, ya samu nasara a matakin karshe na nasarorinsa shida da ya samu a gasar. Pogacar ya lallasa takwaransa dan kasar Denmark da ke rike da kambun Jonas Vingegaard da kuma dan kasar Beljiyam Remco Evenepoel da suka zo na biyu da na uku a matakin karshe na gasar da tazarar mintuna shida da dakika 17.

Rafa Nadal dan kwallon Tennis na duniyaHoto: Jean-Francois Badias/AP/picture alliance

Shahararren dan wasan Tennis din nan Rafael Nadal ya samu koma-baya, a shirye-shiryensa na halartar gasar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle wato Olympics ta 2024 da birnin Paris fadar gwamnatin Faransa ke daukar nauyi. Nadal ya sha kashi a Lahadin karshen mako yayin wasan karshe na gasar Swedish Open, a hannun takwaransa Nuno Borges na Portugal da ci shida da uku da shida da biyu. Dan kasar Spaniyan mai shekaru 38 a duniya da ya fafata a wasansa na farko na neman lashe kambu tun bayan na French Open da ya lashe a shekara ta 2022, sai dai kuma hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

Birnin Paris na shirin karbar bakuncin 'yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na duniyaHoto: Tasos Katopodis/Getty Images

Yanzu haka kwanaki hudu suka rage a fara wasannin na guje-guje da tsalle-tsalle na duniya, a birnin na Paris fadar gwamnatin Faransa. Ranar Jumma'ar dake tafe ne za a fara fafatwa, zuwa 11 ga watan Agustan da ke tafe. Tuni aka daukin matakan tsaro yayin da dubban masu aikin taimako ke ci gaba da gudanar da shirye-shiryen karshe, gabanin fara wannan wasannin da dubban 'yan wasa daga kasashen duniya za su halarta.

'Yan wasan kwallon kafa na kasa na Jamhuriyar NijarHoto: Getty Images/AFP

Hukumar Kula da Kwallon Kafa ta Jamhuriyar NIjar FENIFOOT ta fito da wani tsarin bunkasa wasanin kwallon kafa, inda ta dauki matakin koyi da wasu kasashe da aka samu ci-gaba a wasanin na kwallon kafa. An shirya wasanin da ake gudnarawa a yanzu haka a jihar Tahoua, wadanda suka hada wakilan jihohi guda takwas na kasar. Tuni dai masu sha'awar kwallon kafa a kasar suka nuna jin dadinsu da wannan gasa, koda yake a jihar Tahoua da ke zaman mai masaukin baki suna nuna takaicinsu sakamakon fitar da ita da aka yi daga gasar.