1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Lagos za asake bude jami'o'i da manya-manyan makarantu

Abdoulaye Mamane Amadou
August 30, 2020

Hukumomi a jihar Lagos Najeriya sun bayyana ranar 14 ga watan Satumba a matsayin ranar da za a sake bude jami'o'in kasar da sauran manyan makarantun boko watanni bayan rufe su saboda annobar Coronavirus.

Nigeria Abuja 2014 | Studenten & Ergebnis der Prüfungen
Hoto: Imago Images/Xinhua Afrika

An bayyana ranar 14 ga watan da ke tafe a matsayin na bude manyan jami'o'in jihar da ke Najeriya da sauran makarantun da ake koyar da ilimi mai zurfi, hukumomin jihar sun kuma ayyana ranar 21 ga watan na gobe a matsayin ranar da makarantun firamarai da sakandarai za su sake budewa a matsayin gwaji.

A baya daliban manya-manyan makarantun Najeriya sun gudanar da zanga-zanga don yin kakkausar suka game da matakin gwamnati na ci gaba da kulle makarantun bokon kasar saboda Coronavirus.

Gwamnatin kasar na shirin sake bude filayen jiragenta ga kasashen waje a ranar biyar ga watan Satumba bayan sake dage ranar bisa wasu dalilai.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW