1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya ta ayyana samun 'yancin kai

October 23, 2011

Majalisar wucin gadin ƙasar Libiya ta bayyana samun 'yantar da ƙasar biyo bayan mutuwar tsohon shugaban ƙasar Moammar Gadhafi

Bukukuwan murna a BenghaziHoto: picture-alliance/dpa

Ayyana samun 'yancin ya zo ne a yayin gudanar da shagulgula a birnin Benghazi dake yankin gabashin ƙasar, inda anan ne boren nuna adawa da mulkin Gadhafin ya samo asali. Hakanan birnin ne ke zama cibiyar majalisar wucin gadin ƙasar a Libiya. Ayyana samun 'yanci shi ne matakin farko game shirin gudanar da zaɓuka a ƙasar ta Libiya, bayan watannin da aka yi ana zubar da jini a ƙasar. A jawabin daya yi lokacin bukukuwan, shugaban majalisar wucin gadin ƙasar ta Libiyas Mustafa Abdel Jalel, ya bayyana cewar duk wata gwamnatin da za'a samar nan gaba a Libiya za ta rungumi tsarin musulunci ne a matsayin tushen dokokin ta. A ranar Alhamis da ta gabata ce 'yan tawayen Libiyar dake samun tallafin sojojin ƙawancen tsaron NATO suka yi galaba akan dakarun Gadhafi bayan cafke shi a mahaifarsa dake garin Sirte, inda kuma ya mutu jim kaɗan bayan hakan. Wani binciken da jami'an kula da lafiya suka gudanar, a yanzu ya tabbatar da cewar Gadhafi ya mutu ne sakamakon raunin daya samu daga harbin bindigar da aka yi masa a kai. Tunda farko jami'an gwamnatin wucin gadi suka ce ya mutu ne a lokacin musayar wuta, amma wani hoton bidiyon da aka fitar ya nunar da cewar cafkeshin da aka yi ya sa wasu am,annar cewar da gangan ne aka harbe shi.

Mawallafi: Umar Saleh umar
Edita : Zainab Mohammed Abubakar