1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya ta soma bincike kan cinikin bayi

Gazali Abdou Tasawa
November 19, 2017

Mahukuntan kasar libiya sun sanar a wannan Lahadi da soma bincike a game da batun cinikin bayi da tashar talabijin ta CNN ta nuna a cikin wani rahoton bincike da ta gudanar. 

Libyen Tripoli Migrant nach Rettung durch Küstenwache
Hoto: Reuters/A. Jadallah

 A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na facebook a wannan Lahadi, Ahmed Metig mataimakin Firayin Ministan gwamnatin hadin kan kasar ta Libiya wacce kasashen duniya suka amince da ita, ya nuna takaicinsa da samun labarin cinikin bayin a kasarsa. Ya ce sun sa a gudanar da bincike kan mutanen da ke da hannu a cikin lamarin domin gurfanar da su a gaban kuliya. 

Kasashen duniya da dama ne musamman na Afirka sun nuna takaicinsu bayan bayyanar wannan labari na cinikin bayi a Libiya wanda ya soma haifar da zanga-zanga a wasu kasahen. Tuni ma dai Shugaba mahamadou Issoufou na Nijar ya sanar da saka wannan batu a taron koli na hadin gwiwar Kungiyar Tarayyar Afirka da ta Tarayyar Turai da zai gudana a karshen wannan wata a birnin Abidjan na Côte d 'Ivoire.