Machar ya zargi Kiir da kokarin aiwatar da mulkin kabilanci
September 12, 2025
'Yan adawa a kasar Sudan ta Kudu sun zargi gwamnatin Salva Kiir da yunkurin kafa tsarin mulkin kama-karya mai nasaba da kabilanci, bayan da aka zargi mataimakin shugaban kasarRiek Machar da kitsa hare-hare a Arewa maso gabashin kasar, lamarin da ya kai ga tsige shi daga mukaminsa.
Jam'iyyar SPLM-IO ta Machar ta musanta laifuffukan da ake zargin mambobinta da aikatawa, ciki har da kisan kai da cin amanar kasa da kuma cin zarafin bil adama. Hasali ma, jJam'iyyar ta adawa ta ce zargin, karya ce tsagwaronta da nufin yin kafar angulu ga yarjejeniyar zaman lafiya.
Karin bayani: Fargabar rinchabewar rikicin Sudan ta Kudu
Dama dai, daurin talala da aka yi wa Riek Machar tun watan Maris ya haifar da fargabar sake faruwar yakin basasa da ya taba barkewa tsakanin 2013 zuwa 2018 a Sudan ta Kudu.
Rikicin dai ya samo asali ne sakamakon takun saka tsakanin kabilu biyu masu biyayya ga shugabannin biyu wato Nuer na Machar da kuma kabilar Dinka ta shugaban kasa Salva Kiir.