1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron ya yabi sojojin Faransa a waje

Yusuf Bala Nayaya
December 23, 2018

Shugaba Emmanuel Macron da yake jawabi ga sojoji 1000 a birnin N'Djamena ya ce duk inda Faransa ke yakar 'yan ta'adda kare kanta take yi.

Niger - Macrons Truppenbesuch
Hoto: Getty Images/AFP/L. Marin

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya gana da dakarun kasar ta Faransa a kasar Chadi inda ya yaba masu kan irin gudunmawar da suke bayarwa wajen yaki da 'yan ta'adda a yankin.

Da yake jawabi ga sojoji 1000 a birnin N'Djamena ya ce duk inda Faransa ke yakar 'yan ta'adda kare kanta take domin irisu ne suka kai hari a birnin Strasbourg.

Faransa dai na da dakarun soja 4,500 wadanda ke aiki cikin rundiyar Barkhane masu yakar 'yan ta'adda a Chadi da Mali da Burkina Faso da Mauritaniya da Mali da Nijar.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW