1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kolin Afirka da Faransa a Kenya

Abdourahamane Hassane
May 6, 2026

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron zai fara wani sabon rangadi a nahiyar Afirka.

Emmanuel Macron
Emmanuel MacronHoto: Karen Minasyan/AFP

Shugaban zai kai ziyara ne saboda  taron kolin Afirka da Faransa  da za a yi, a Kenya, karo na farko da za a yi shi  a ƙasar da ke amfani da Turancin Ingilishi, tare da mai da hankali sosai kan zuba jari a fannin tattalin arziki.

 Taron koli  na birnin  Nairobi, wanda aka yi wa lakabi da"Africa Forward"a Turance, zai zama na farko a ƙarƙashin jagorancin shugaban Faransa da zai haɗa sauran shugabannin ƙasashe da gwamnatocin tun lokacin da ya hau mulki a shekarar ta 2017.

Kafin ya isa Kenya, Macron zai tsaya a Masar a ranar Asabar, inda shi da takwaransa Abdel Fattah al-Sisi za su bude Jami'ar Senghor Francophone a birnin Alexandria.